WAKA A BAKIN MAI ITA – KARYA SU KEYI BABU MAI CUTAR COVID-19 A JIHAR KOGI – GWAMNA BELLO

KARYA SU KEYI BABU MAI CUTAR COVID-19 A JIHAR KOGI – GWAMNA BELLO

Gwamnatin Jihar Kogi ta karyata hukumar NCDC da ta sanar da cewa an samu mutum biyu masu dauke da cutar korona a karon farko a Jihar.

Kwamishinan lafiya na Jihar, Dakta Saka Haruna Audu ne ya karyata hukumar NCDC din a madadin gwamna Yahaya Bello a wata takardar sanarwar manema labarai da ya sake a ranar Laraba, inda ya ce, zancen nasu karya ne.

Ya ce: “Jihar Kogi har zuwa yanzu ba ta da mai dauke da cutar Korona. Mun samar da tsarin yin gwaji sosai, wanda kuma an yi gwaje-gwajen amma har yanzu babu wanda ke dauke da wannan cuta.

“Mun sanar tun da dadewa cewa babu wanda zai sa mu yi karya wurin ayyana cutar Korona a jihar Kogi alhali babu mai ita.

“Sannan kuma babu wanda ya isa ya tursasa mana sanar da kamuwa da cutar alhali karya ne. Ba za mu lamunta ba.” inji shi

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *