FAFATAWÀR NASARAWA UNITED DA KANO PILLARS YA BURGE JAMA’A

An fafata tsakanin kungiyar Nasarawa United da Kano pillars

Daga Zubairu M Lawal Lafia

A ranar lahadin da ta gabata ne aka cigaba da gasar kwallon kafa ta gida Nijeriya gasar da ake kira da suna ( Nigeria Premier League).

An fafata tsakanin kungiyar Nasarawa United da takwararta ta Kano pillars a filin wasa ta Lafia dake bukkan sidi.

Wasan da aka je hutun rabin lokaci babu wanda ya jefa kwallo a ragar wani tsawan minti 45 bayan dawowa hutun Kungiyar Kano pillars ta sauya yan wasa biyu na gaba cikin minti daya da shigarsu sai ga Kwallo a ragar Nasarawa United. Ta kafar Nwagua Nyima.

Ana gab da tashi cikin minti 82 Adamu Hassan ya zura kwallo a ragar Kano pillars inda aka tashi 1-1.

Dukkanin masu horar da yan wasan sun yabawa yan wasan su saboda kwazo da bajintar da suka nuna wajen murza Kwallon .

A filin wasan an tsaurara matakan tsaro na hana yan kallo shiga filin wasan saboda matakan dakile yaduwar annobar cutar Korona bairus.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *