Da gaske ne EFCC ta samu kudi a gidan Lawal Daura?

Ranar 7 ga watan Agusta ne dai mukaddashin shugaban Najeriya, Yemi Osinbajo ya kori Lawal Daura daga mukamin shugaban rundunar tsaro ta farin kaya (DSS) bayan jami’an hukumar sun hana sanatocin Najeriya shiga majalisa.

Mukaddashin shugaban kasar ya yi tir da aikin da ya bayyana cewa ya ci karo da tsarin mulkin Najeriya tare da shan alwashin ganowa da hukunta wadanda ke da hannu a aikin.

Da yammacin ranar ne dai Osinbajo ya gana da sabon shugaban hukumar da ya maye Daura, Matthew B. Seiyefa, da kuma shugaban hukumar EFCC mai yaki da masu yi wa tattalin arzikin Najeriya zagon gasa, Ibrahim Magu.

Washe gari dai rahotanni sun ce jami’an hukumar EFCC sun kai samame gidan tsohon shugaban hukumar DSS, Ita Ekpeyong.

Bayan nan kuma aka fara yada wani bidiyo a shafukan sada zumunta wanda ake ikirarin cewar bidiyon kudin da aka samu a gidajen Tsohon shugaban DSS, Lawal Daura ne.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *