‘City ba za ta sayi dan wasa ba a Janairu’
Daga Ibrahim Lawal
A ranar Litinin ne Manchester City za ta kara da Wolverhampton Wanderers a karashen wasan mako na 22 a gasar Premier A Ettihad.
City tana ta biyu a kan teburin Premier da maki 50 da tazarar maki bakwai tsakaninta da Liverpool ta daya, wadda ta buga karawa ta 22 a ranar Asabar.
Liverpool ta yi nasarar cin Brighton daya mai ban haushi, kuma Mohamed Salah ne ya ci kwallon a bugun fenariti.
Pep Gaurdiola ya ce ba za su sayo dan kwallo ba a watan nan na Janairu, sai idan ta kama za su iya dauka aro na karamin lokaci.
Kocin ya kara da cewar a irin wannan lokacin ba za ka samu dan wasa mai kwari ba, domin kowacce kungiya ba ta son rabuwa da manyan ‘yan kwallonta domin kakar wasa ta yi nisa.