TASHIN HANKALI – Mahara sun kashe mutum 15 a Nasarawa

Mahara sun kashe mutum 15 a Nasarawa

Daga Zubairu  M Lawal

Wasu mahara da ba’asan ko suwayeba sun kashe mutani 15 yan kabilar Mada a kauyen Numa dake karamar Hukumar Akwanga a jihar Nasarawa.

Bayan wanan kisan gillar gungun matasa yan kabilar Mada sun gudanar da zanga zangar rashin amincewa da wanan lamarin .
Da yake jawabi na kwantar da hankalin alumman garin Akwanga Dan Majalisar Dattijai mai wakiltar mazaver Akwanga Nasarawan Eggo da Wamba ,

Sanata Philip Aruwa Ginka yayi kira ga alumman Mada da sauran Jama’a cewa kowa ya kwantar da hankalinsa .Gwamnati zata binciko wadanda suka aikata wanan laifin kuma a hukuntasu.

Ya kara da cewa yaji dadi da yadda matasa basu dauki Doka a hannu ba kuma basu farma kowa ba suka gudanar da zanga zangar lumana.

Shima a nasa jawabin Shugaban Matasan yan kabilar Mada Kyune Umaru ya dai zargi yan kabilar Fulani da ba’a ga maciji da aikata wanan ta’assar.na kisan wadanda basuji ba . kuma basu gani ba.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *