ABIN TAUSAYI – Masu garkuwa sun shiga gidan mutuwa sun yi awon gaba da duka masu zaman makoki a Katsina

Masu garkuwa sun shiga gidan mutuwa sun yi awon gaba da duka masu zaman makoki a Katsina

Rahotanni da dumi-duminsu daga jihar Katsina suna bayyana cewa a daren jiya Talata yan bindiga sun shiga cikin wani gidan makoki a garin Kofa dake cikin karamar hukumar Kusada sun yi awon gaba da mutane dake zaman ta’aziyya.

Daga cikin mazauna yankin ya bada labari inda Isah Ibrahim ya rubuta karin bayani a shafinsa na Facebook cewa:-

“Innalillahi wa’innah ilaihir raji’un

Cikin dare’ n nan masu garkuwa da jama’a sun shiga cikin garin Kofa dake karamar hukumar Kusada, jihar katsina, inda suka rufta gidan makoki suka tarkata masu zaman makokin suka korasu daji.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *