Wasu ƴan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun sace sarkin Fulanin Bungudu, da ke jihar Zamfara a arewacin Najeriya, mai martaba Alhaji Hassan Attahiru.
Ƴan bindigar sun sace sarkin ne kan hanyarsa daga Kaduna zuwa Abuja, kamar yadda ɗaya daga cikin ƴaƴansa da kuma basaraken masarautar Zannan Bungudu Hon Abdulmalik Zubairu ya tabbatarwa BBC Hausa.
Bayanai sun ce an kashe ɗaya daga cikin jami’in ƴan sanda a musayar wutar da ƴan bindigar suka yi jami’an tsaron da ke tare da sarkin cikin mota a hanyar Abuja.
Karin bayani na tafe..
