Dakarun sojin Nijar da suka yi wa gwamnatin farar hula ta Mohammed Bazoum juyin mulki na kira ga ƙasar Rasha da ta kawo musu dauki, tare da neman ƙasar Faransa da sauran ƙasashen yamma da ke ƙasar da su fice da Nijar ɗin.
Cikin wata sanarwa ta kakakin majalisar ceto ƙasar ta sojoji Kanal Manjo Amadu Abdurahamane, ya karanta a gidan talbijin na ƙasar ya yi kira ga ƙasar Rasha da ta taimaka wa Nijar da sojoji da kayan aiki.
A yau ne ƙungiyar Ecowas ke gudanar da taro don tattauna batun juyin mulkin da sojojin suka yi a Nijar.
To sai dai cikin sanarwar da majalisar ceton ta Nijar ta fitar, ta yi zargin cewa taron na Ecowas yunƙuri ne far wa Nijar da yaƙi.
A don haka ne ma Kanal Manjo Amadu Abdurahamane ya ce a shirye suke su kare ƙasarsu daga hare-haren da ya yi zargin Ecowas za ta ƙaddamar wa ƙasar.
Sannan kuma ya yi kira ga ‘yan ƙasar da su fito su gudanar da zanga-zanga domin mara musu baya.