Gwamnatin Nasarawa zata dauki mataki kan zubda Bola a magudanan ruwa

Gwamnatin Nasarawa zata dauki mataki kan zubda Bola a magudanan ruwa

Daga Zubairu Lawal
Gwamnatin Nasarawa zata dauki mataki kan masu zuba shara a magudanar ruwa.
Kwamishinan tsaftar muhali ta jihar Hon.Kwanta Yakuba ya bayyana a lokacin da yake zantawa da manema Labarai bayan kammaka dokar shara na karshen wata da Gwamnatin jihar ta tsara.
Kwamisinan yace; Gwamnatin jihar bazata zura ido ta kyale masu zubar da shara a Magudanan ruwa da yake toshe banyan ruwa ya kuma haifar da ambaliyan ruwa a gariba.
Yace; zuba shara a kwalbati magudanan ruwa yana haifar da ambaliyan ruwa, Wanda ke sanya ruwa ke shiga gidajen al’umma.
Kwamishinan yace; dokar da Gwamnatin jihar Nasarawa ta tsara kan tsaftar muhalli yana samun karbuwa cikin fadin jihar.
Yace; duk da ana kama masu kunnin kashi amma yanzu dadama mutani suna kiyayewa suna zama a gidajensu suna tsaftace gidajensu.
Kwamishinan Kwanta Yakubu ya yqbawa Sarkin Lafia mai shari’a Sidi Bage danane da goyon baya da yakeba wannan kuddurin na tabbatar da jama’a sun tsaftace gidajensu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *